Yanbindiga sun yi garkuwa da mutum bakwai a bayan kashe guda a jihar Ogun

Spread the love

Mutum ɗaya ya mutu a jihar Ogun da ke kudancin Najeriya yayin da ‘yanbindiga suka yi garkuwa da mutum bakwai, a cewar rundunar ‘yansanda a jihar.

Wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce lamarin ya faru ne ranar Lahadi a kan babban titin Sagamu-Ijebu-Ode.

Maharan da suka kai kusan bakwai, sun isa wurin ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47, in ji sanarwar da kakakin ‘yansanda Omolola Odutola ya fitar a yau Talata.

Ya ƙara da cewa sun bayyana lamarin a matsayin fashi da makami, da kisan kai, da kuma garkuwa da mutane.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *