Yau Ake Daura Auren Sadiya Haruna A Karo Na 9

Spread the love

A Juma’ar nan, 5 ga watan Yuli, 2024, jarumar TikTok, Sayyadda Sadiya Haruna, za ta amarce a karo na tara.

A safiyar Juma’ar Sadiya Haruna ta dora katin gayyatar daurin auren nata, wanda zai gudana a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Auren Sayyada Haruna da angonta mai suna Hon. Babagana Audu Grema na zuwa ne ’yan watanni ƙalilan bayan kotu ta raba aurenta da tsohon mijinta, shahararren dan TikTok, G-Fresh Al-Amin.

Auren Sadiya Haruna da G-Fresh dai bai yi tsawon kwana ba, inda takaddama ta rika dabaibaye zaman nasu, har a karshe suka kare a gana kotun Musulunci.

Dambarwar auren Sadiya Haruna da G-Fresh ta karaɗe kafofin sada zumunta inda ake ta ce-ce-ku-ce a kai, kafin daga karshe kotun ta raba auren.

Mako guda ke nan da Sadiya Haruna ta yi wa G-Fresh wankin babban bargo a lokacin da aka karbi bakuncinta a shirin tattauna na Gabon’s Talk Show, na tauraruwar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon.

Aminiya ta ruwaito cewa a ranar Juma’ar ce kuma za a daura auren takwarar Sayyada, wato Sadiya Gyale a Jihar Kano.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *