Za A Fara Ɗaukar Sabbin Jami’an Hukumar Shige Da Fice Da Na Kashe Gobara A Augusta

Spread the love

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa za a fara ɗaukar ma’aikatan Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa da Hukumar Kashe da Gobara ta Tarayya a watan Agusta.

Sakataren Hukumar Shige da Fice, Gyaran Hali da Hukumar Kashe Gobara, Jafaru Ahmed ne, ya bayyana haka a wata sanarwa.

Ahmed ya bayyana cewa, za a fara neman gurbin aikin ne a ranar 15 ga watan Yuni, 2024 zuwa ƙarshen watan Satumban 2024.

Ya tabbatar da cewa za a fitar da sunayen waɗanda suka yi nasara a matakin farko, ta hanyar tuntuɓar su kafin zuwa mataki na gaba.

Ya nemi afuwa kan jinkirin fara

ɗaukar ma’aikatan kamar yadda aka tsara a baya.

Jinkirin ya faru ne saboda gudanar da binciken ma’aikatan wasu hukumomin da ke ƙarƙashin babbar hukumar.

Binciken ma’aikatan ya shafi Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, Hukumar Kashe da Gobara ta Tarayya da Hukumar Kare Farar Hula ta Najeriya.

Duk da jinkirin, Ahmed ya tabbatar da cewa duk waɗanda suka yi nasara za su samu bayanin matakai na gaba kan abin da za a yi, ta wayoyinsu ko imel ɗinsu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *