Za a fara biyan masu sanya bidiyo a Facebook a Ghana

Spread the love

Masu ƙirƙirar bidiyo don wallafawa a dandalin sada zumunta na Meta a Ghana na ci gaba da bayyana murnarsu, kan matakin kamfanin na amincewa a fara biyan ƴan ƙasar masu ɗora bidiyo a shafinsu na Facebook.

Daman tun a baya kamfanin na Meta mai Facebook da Instagram da WhatsApp ya sanar da cewa daga ranar 1 ga watan Yuli na 2024 zai fara biyan wadanda suka cancanta, da ke sanya hotunan bidiyo a shafukansu na Facebook.

Ana sa ran wannan matakin zai haifar da bunƙasar tattalin arziki, tare da samar da dubban ayyuka ga mutane musamman matasa yayin da ake fuskantar matsanancin rashin aikin yi a kasat ta yammacin Afirka.

An dade ana fatan ganin ranar da daya daga cikin manyan kamfunan sada zumunta a duniya na Facebook zai fara biyan `yan kasar ta Ghana masu kirkiro bidiyo suna dorawa a kan shafin.

Dubban matasa ne a Ghana suka rungumi sana`ar kirkiro bidiyo suna wallafawa a kan intanet don rufa wa kai asiri yayin da matsalar rashin aiki ta yi kamari.

Duk da yake masana na son barka da wannan cigaba amma suna kiran gwamnati da ta kara jajircewa a wajen sa ido a kan irin abubuwan da masu kirkio bidiyo za su rinka dorawa a kan shafukansu.

Musamman yayin da ake shirin gudanar da babban zaben kasar ta Ghana a watan Disamba mai zuwa, ganin cewa wasu ka iya amfani da wannan dama wurin yada farfaganda ko labaran kanzon-kurege da cin zarafi, ko kyama, wanda haka zai iya janyo tarzoma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *