Za a yi wa ‘yan takarar zaɓen ƙananan hukumomi gwajin ƙwaya a Kano

Spread the love

Shugaban hukumar zaɓe na jihar Kano, Farfesa Sani Lawal Malumfashi, ya ce sai an yi wa kowanne ɗan takara a zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a yi gwajin ƙwaya kafin a bashi damar tsayawa takara.

Farfesa Malumfashi, ya sanar da hakan ne a yayin wani taron manema labarai da hukumar ta gudanar a Kano a ranar Alhamis.

A yayin taron, hukumar zaben ta sanar da cewa duk mai son tsayawa takarar shugaban ƙaramar hukuma a zaɓen to zai sayi fom a kan naira miliyan 10.

Yayin da ɗan takarar kansila kuma kuɗin fom ɗinsa ya kama naira miliyan biyar.

Za a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin jihar ne a ranar 30 ga watan Nuwambar 2024.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *