Za mu fara rushe katangar gidan sarki na Nassarawa – Gwamnatin Kano

Spread the love

Gwamnatin jihar Kano Abba Kabir ,a arewacin Najeriya ta ce za ta fara aikin rushe katangar gidan Sarki na Nasarawa da Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ke ciki, tana mai cewa “saboda ya lalace”.

Gwamnatin ta kuma umarci kwamishinan ‘yansandan jihar da ya fitar da Aminu Ado daga gidan bayan hukuncin kotu a yau Alhamis, wanda ta yi iƙirarin cewa ya ba ta nasara a kan ɓangaren da suka shigar da ƙarar.

Kwamashinan Shari’a na Kano Haruna Isa ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da ya gudanar a gidan gwamnati, inda ya jaddada cewa bangon ƙaramin gidan sarkin da ke ƙwaryar birnin Kano ya lalace.

“Mun kammala shirye-shirye domin rushewa da kuma sake gina katangar da ta lalace nan take,” in ji shi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *