Za Mu Ɗauki Mataki Idan Zanga-Zanga Ta Wuce Gona Da Iri — Sojoji

Spread the love

Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, ya ce sojoji za su dauki muddin zanga-zangar tsadar rayuwa da ke ci gaba da gudana a faɗin ƙasar ta wuce gona da iri.

Janar Musa ya bayyana hakan ne yayin da yake gargadin masu fakewa da zanga-zangar suna ɓarna da sace-sacen kayan gwamnati da al’umma.

Ana iya tuna wasu bata-gari sun fake da zanga-zangar wajen wawushe kayayyaki a wata cibiyar Hukumar Sadarwa ta Nijeriya NCC tare ƙona wasu sassanta a jihar Kano.

Wasu bayanai na cewa an shirya ƙaddamar da cibiyar fasahar sadarwa a mako mai zuwa.

Janar Musa ya kara da cewa gwamnati na bakin kokarinta wajen magance matsalolin tattalin arziki da ke damun kasar, yana mai kira ga jama’a da su riki gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi da alhakin nauyinsu.

 

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *