Wata babbar kotu a Abuja ta bayar da belin tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Alhaji Yahaya Bello a kan kuɗi Naira miliyan 500 bisa zargin karkatar da kuɗaɗen gwamnati.
Mai shari’a Maryanne Aninih ce ta bada umarnin a ranar Alhamis ta kuma umurci Bello da ya gabatar da waɗanda za su tsaya masa guda uku a daidai wannan adadin kuɗin.
Alƙalin ta ce dole ne waɗanda za su tsaya masa su kasance fitattun ’yan Najeriya da ke da kadarori a ɗaya daga cikin unguwannin Maitama da Jabi da Utako da Apo da Guzape da Garki da Asokoro.
Alkalin ta kuma buƙaci Yahaya Bello da ya ajiye fasfo ɗinsa da sauran takardun tafiye-tafiye a wurin magatakardar kotun
Ta kuma bayar da umarnin cewa dole ne ya ci gaba da zama a gidan gyaran yarin Kuje har sai an cika sharuɗɗan belin.
Mai shari’a Maryann Anenih, a ranar 10 ga watan Disamba, ta ƙi amincewa da buƙatar belin tsohon gwamnan, tana mai cewa an shigar buƙatar ne da wuri.
- Kungiyar Rayuwa Deployment Association (RADA) Ta Kudiri Aniyar Nema Wa Matan Da Aka Ci Zarafin Su Mafita.
- Yan Majalissar Wakilai Za Su Ba Wa Shugaba Tinubu Miliyan 704.91 Don Tallafawa Yan Nigeria