Ɗan Najeriyar da ke shirin kafa tarihi a Gasar Olympics ta 2024

Spread the love

A yayin da zakaran wasan Badminton na Afirka Anuoluwapo Juwon Opeyori ke shirin kafa tarihi a gasar Olympics a birnin Paris, ɗan Najeriyar na jin cewa ya yi abubuwan bajinta.

Duk da cewa an haife shi a wani ƙauye a Lagos, mafi cunkoso a Najeriya, ɗan wasan mai shekara 27 ya lashe kofin nahiyar guda huɗu, fiye da kowane ɗan Afirka a baya.

Abin da ya ƙara ɗaukar hankalinsa shi ne, yana zaune ne a ƙasar da babu wani wurin da aka gina don wasan Badminton, amma duk da haka yana fatan zama ɗan Afrika na farko da zai samu ci gaba a gasar ta Olympics.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *